Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya sake jaddada matsayar kasarsa kan rikicin Gaza, yana nuna goyon bayansa ga kokarin kawo karshen kisan kiyashi da kuma tabbatar da zaman lafiya, yayin wata tattaunawa da Shugaban Brazil, Luiz Inacio Lula da Silva, inda ya yaba wa Brazil kan tsayuwarta tsayin daka wajen kare hakkin Falasdinawa.
Erdogan ya ce Turkiyya za ta ci gaba da daukar dukkan yarjejeniyoyin zaman lafiya a Gaza da muhimmanci, tare da aiki don kawo karshen bala’in jin kai, kafa zaman lafiya da sake gina yankin Falasdinawa.
Ya gode wa Brazil saboda rashin yin shiru kan abin da ya kira kisan kiyashin da Isra’ila ke yi. A halin yanzu, hare-haren Isra’ila sun kashe sama da Falasdinawa 71,000 tun 2023, tare da lalata mafi yawan kayayyakin more rayuwa a Gaza, yayin da keta yarjejeniyar tsagaita wuta ke kara jawo asarar rayuka da hana shigar da kayan agaji.














