Afirka

Yaƙin Sudan: Sojojin sun ce sun yi wa sojojin RSF lugude a Darfur da Kordofan

Sojin Sudan sun ce aikin da suka yi ta sama da ƙasa sun lalale ɗaruruwan motoci a cikin mako guda.

Newstimehub

Newstimehub

9 Jan, 2026

1767974530083 wubupc e8ccba2581251ce33622a6a0cedbf7eacf99e81e97bfdf779242b36e779832cc

Sojojin Sudan sun ce sun yi wa Rundunar ‘Yan Sa-Kai ta RSF mummunar asara ta sama da ƙasa a yankunan Darfur da Kordofan a makon da ya gabata. A cewar wata sanarwa, harin ya lalata kusan motocin yaki 240 tare da kashe ɗaruruwan mayaƙan RSF.

Rundunar ta ce harin ya shafi wuraren ajiya, kayayyakin sufuri, da wuraren jiragen sama marasa matuki, ciki har da Filin Jirgin Sama na Nyala a Kudancin Darfur. Sojojin ƙasa sun kuma ce sun kori mayaƙan RSF daga yankuna da dama, yayin da ake ci gaba da bin sauran.

RSF ba ta fitar da wata sanarwa ba game da ikirarin sojojin. A halin da ake ciki, rikicin ya tilasta wa dubu-dubban fararen hula yin hijira, yayin da matsalar jin ƙai ke ƙara ta’azzara tun bayan fara yaƙin a watan Afrilu 2023.

Majiyar Labari: TRT HAUSA