Ba tare da hayaniya ba amma da tasiri mai zurfi, Isra’ila ta sake aika saƙo mai ƙarfi game da matsayinta a rikicin Gaza, yayin da ministan tsaron ƙasar ya bayyana cewa sojojin Isra’ila ba za su janye gaba ɗaya daga zirin ba.
Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ce sojojin ƙasar ba za su fice baki ɗaya daga zirin Gaza ba, matakin da ake ganin zai iya kawo cikas ga shirin Amurka na samar da zaman lafiya a yankin.
A jawabin da ya gabatar ga shugabannin yankunan da Yahudawa ‘yan kama wuri zauna, Katz ya ƙara da cewa idan lokaci ya yi, za a kafa rundunar tsaron Isra’ila a yankin maimakon a zaɓi shugabanci daga cikin Falasdinawan da suka rasa muhallansu.
Wannan mataki na nufin tabbatar da zama na dindindin ga ‘yan kama wuri zauna da ke yankin tun sama da shekaru 20. Firayim Minista Benyamin Netanyahu ya sha nanata aniyarsa ta faɗaɗa matsugunan Yahudawa a zirin Gaza, duk da ƙorafe-ƙorafen ƙasashen duniya.














