Wani jirgin ruwa da ke ɗauke da kusan mutane 50 tare da kayayyakinsu ya kife a daren Alhamis a Kogin Niger a arewacin Mali, lamarin da ya yi sanadin mutuwar wasu fasinjoji tare da ɓacewar wasu, kamar yadda hukumomin yankin suka tabbatar.
Gwamnan yankin ya bayyana cewa binciken farko ya nuna hatsarin ya faru ne sakamakon rashin bin ƙa’idojin zirga-zirgar ruwa, tare da asarar dukiya mai yawa. Kogin Niger na taka muhimmiyar rawa a matsayin babbar hanyar sufuri ga al’ummomin da ke zaune a bakin ruwa, musamman a arewacin ƙasar.
Lamarin ya faru ne a daidai lokacin da Mali ke fuskantar ƙalubalen tsaro tun daga 2012, sakamakon hare-haren ƙungiyoyin ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka, wanda ke ƙara haɗarin tafiye-tafiye da rayuwar fararen hula.














