Gwamnatin Somaliya ta sanar da soke dukkan yarjejeniyoyin da suka shafi hukumomin tarayya, gwamnatocin jihohi da cibiyoyin da ke aiki a cikin ƙasar, tana mai cewa an nuna rashin mutunta ikon ƙasar da cikakkar ‘yancinta. Wannan mataki ya biyo bayan matakin da Isra’ila ta ɗauka na amincewa da Somaliland a matsayin ƙasa mai zaman kanta, alhali Mogadishu na ɗaukar yankin a matsayin wani ɓangare na Somaliya.
A cikin wata sanarwa ta hukuma, gwamnatin Somaliya ta ce tana da sahihan rahotanni da hujjoji da ke nuna ayyuka masu barazana ga haɗin kan ƙasar da ‘yancinta na siyasa. An ambaci tashoshin jiragen ruwa na Berbera, Bosaso da Kismayo a matsayin muhimman wuraren da ake zargin an kulla yarjejeniyoyi ba tare da izinin gwamnatin tarayya ba.
Haka kuma an ambaci Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), inda ake zargin ta taimaka wajen jigilar wani shugaban ‘yan aware na Yemen zuwa Abu Dhabi ta hanyar amfani da filayen jiragen sama da tashoshin ruwan Somaliya ba tare da izini ba. Gwamnati ta ce ta buɗe bincike kan wannan zargi.
Somaliland, wacce ta ayyana ‘yancinta tun 1991, na gudanar da harkokinta a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta, kuma tana da muhimmiyar matsayi a mashigar Bab-el-Mandeb, wuri mai matuƙar muhimmanci ga zirga-zirgar kasuwanci da tsaro a Kahon Afirka. Shugaban Somaliya, Hassan Sheikh Mohamud, ya bayyana amincewar Isra’ila da Somaliland a matsayin “barazana” ga zaman lafiyar yankin.
Duk da haka, Mogadishu ta ce har yanzu tana maraba da haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa, muddin ana mutunta ikon Somaliya, haɗin kan ƙasarta da dokokin ƙasa da ƙasa. Ma’aikatar Harkokin Waje ta samu umarnin sanar da dukkan ƙasashen da abin ya shafa tare da aiwatar da matakin.














