A wani babban wasan ƙarshe da ya cika da tashin hankali da zazzafar fafatawa, ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Senegal ta doke mai masaukin baki Maroko da ci 1-0 a birnin Rabat, inda ta ɗauki kofin AFCON 2025 a karo na biyu a tarihinta.
Wasan ya yi cike da ce-ce-ku-ce, musamman bayan da alkalin wasa ya bayar da bugun fenareti ga Maroko a mintuna na ƙarshe, abin da ya sa ‘yan wasan Senegal suka nuna rashin amincewa ta hanyar barin fili na ɗan lokaci. Duk da haka, bayan dawowarsu, an sake duba hukuncin ta hanyar VAR, kuma an tabbatar da bugun fenaretin, sai dai Brahimi Diaz ya kasa cin ƙwallon bayan Edouard Mendy ya cafke bugunsa.
Senegal ta ci kofin AFCON 2025 bayan Pape Gueye ya zura ƙwallo a minti na 94 na ƙarin lokaci, inda suka doke Maroko da ci 1-0. Duk da samun bugun fenareti, Maroko ta kasa ramawa bayan mai tsaron ragar Senegal ya hana su cin ƙwallo, lamarin da ya ba Teranga Lions damar kammala gasar da nasara.














