Kasa da makonni biyu bayan rantsar da shi a matsayin shugaban ƙasa, Mamady Doumbouya ya tabbatar da Amadou Oury Bah a matsayin Firayim Ministan Guinea, matakin da ke nuna ci gaba da tsari a sabuwar gwamnatin da ta biyo bayan zaɓen da ya gudana a ƙarshen Disamba.
A wata sanarwa da aka karanta a talabijin na ƙasa, Doumbouya ya ce Bah, wanda ya riƙe muƙamin firayim minista tun daga Fabrairu 2024 a lokacin mulkin rikon ƙwarya, zai ci gaba da jagorantar gwamnati. Shugaban ya kuma bayyana cewa za a kafa ma’aikatu 27 da sakatarori-janar guda biyu, yayin da ake sa ran bayyana sunayensu nan ba da jimawa ba.
Doumbouya, wanda ya karɓi mulki bayan juyin mulki a 2021, ya fara wa’adinsa na shekaru bakwai a ranar 18 ga Janairu, bisa sabon kundin tsarin mulki da aka amince da shi a kuri’ar raba gardama a 2025, wanda ya tsawaita wa’adin shugaban ƙasa daga shekaru biyar zuwa bakwai.














