Afirka Tsaro

’Yan Bindiga Sun Kashe Sojojin Libya Uku Kusa da Iyakarta da Nijar

Harin ’yan bindiga a kudancin Libya ya kashe sojoji uku a kusa da iyakar Nijar, lamarin da ya ƙara nuna rashin tsaro a yankin kan iyaka.

Newstimehub

Newstimehub

3 Feb, 2026

b6a7503b450361582c2671a0d3876456d4ec1f2ea7b08f5a3222f29065907a1f

Sojojin gabashin Libya sun ce ’yan bindiga sun kashe sojoji uku tare da jikkata wasu a wani hari da aka kai kudancin ƙasar, kusa da kan iyakarta da Nijar. Harin ya faru ne a kusa da wurin ƙetare kan iyaka na Al-Toum, inda aka kuma kama wasu sojoji, a cewar sanarwar rundunar.

Sanarwar ta ƙara da cewa ’yan bindigar sun kai hare-hare a yankunan Wadi Bougrara da Salvador, dukansu kusa da kan iyaka da Nijar. Rundunar ta bayyana maharan a matsayin ƙungiyoyin aikata laifuka da ke safarar mutane da kayayyaki ba bisa ƙa’ida ba, waɗanda ke aiki a yankunan hamada da ke kan iyaka.

A cewar sojojin, dakarun tsaro sun sake karɓe ikon wuraren da aka kai harin tare da bazama domin farautar maharan. Rundunar ta ce akwai alamun cewa ’yan bindigar sun tsere zuwa cikin Nijar bayan kai harin.

Tun da fari, wata ƙungiya da ta kira kanta “‘Yan juyin juya hali na Kudu” ta yi ikirarin cewa ta kwace ikon wurin ƙetare kan iyaka na Al-Toum. Hukumomin Libya sun ce ana ci gaba da aikin tsaro domin dakile barazanar da ke fitowa daga yankin kan iyaka.

Majiyar Labari: TRT HAUSA