Ministan ma’adinai na Democratic Republic of Congo, Louis Watum, ya yi watsi da zargin cewa ƙasar ta sayar da albarkatun ma’adinanta ga United States.
Watum ya ce yarjejeniyar da aka kulla a Disamba ta bai wa kamfanonin Amurka damar shiga tattaunawa kan ayyukan zuba jari ne kawai, ba sayar da ma’adanai ba. Yarjejeniyar ta shafi ma’adinai masu muhimmanci kamar copper, cobalt, coltan da lithium, tare da haɗa yunƙurin diflomasiyya na samar da zaman lafiya a gabashin ƙasar.
Ministan ya jaddada cewa duk wani zuba jari zai gudana ne bisa dokokin ma’adinai na ƙasar, yana mai cewa har yanzu yawancin albarkatun DRC ba a bunƙasa su ba.
Ya kuma ce Kinshasa ba ta damu da takun-sakar siyasa tsakanin Amurka da China ba, illa dai mayar da hankali kan ci gaban cikin gida, ciki har da samar da ayyukan yi da ilimi. DRC na daga cikin ƙasashen da ke da manyan ma’adanai a duniya, kuma tana taka muhimmiyar rawa a kasuwar cobalt ta duniya.
Majiyar Labari: TRT AFRIKA














