Gabas Ta Tsakiya

NATO ta kakkaɓo makami mai linzami na Iran da aka harba Turkiyya

Ankara ta ce a shirye take ta kare tsaron ƙasarta a yayin da ta keci gaba da neman salama da aminci.

Newstimehub

Newstimehub

4 Mar, 2026

2964967c0d07896f0f1b6dd23d1ca1ee7563f4aadc2889211ac09671a6a16f64

A cewar jami’an Ma’aikatar Tsaron Turkiyya a ranar Laraba, na’urorin kariyar sararin samaniya na NATO sun tsinkayi tare da harbo wani makami mai linzami na Iran da ke kan hanyar faɗawa Turkiyya.

An tsinkayi makamin ne a wajen sararin samaniyar Turkiyya bayan ya ƙetare yankunan Iraƙi da Siriya.

Ma’aikatar Tsaron Turkiyya ta ce wani ɓangare na na’urar kariyar da aka yi amfani da ita wajen daƙile makami mai linzamin ya fadi a gundumar Dortyol a lardin Hatay.

Ba a samu asarar rai ko raunuka ba.

Ankara ta ce niyyarta da ƙarfinta na kare tsaron ƙasa suna kan mataki mafi girma, ta jaddada cewa yayin da Turkiyya ke goyon bayan zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, tana da cikakken ikon kare yankinta da ‘yan ƙasarta daga kowace barazana.

Hukumomi sun yi gargaɗi cewa za a mayar da martani mai ƙarfi ga duk wani mataki da aka ɗauka na kai mata hari mata, kuma sun yi kira ga dukkan ɓangarori da su guji matakai da za su iya ƙara faɗaɗa rikicin.

Turkiyya ta ƙara da cewa za ta ci gaba da tattaunawa da NATO da abokan ƙawance.

“Muna maimaita gargaɗinmu ga dukkan ɓangarori da su guji matakai da za su iya ƙara tashin hankali a yankin kuma su haifar da yaduwar rikice-rikice a fadin wani yanki mai faɗi,” kamar yadda Burhanettin Duran, Shugaban Harkokin Sadarwa na Turkiyya, ya ce a cikin wata sanarwa.

Ya kuma roƙi masu amfani da kafafen sada zumunta da su guji yaɗa bayanai marasa tabbaci.