Wani babban jami’in tsaron Iran, Ali Larijani, ya yi ikirarin cewa fiye da sojojin United States 500 ne aka kashe tun bayan fara rikicin da ya barke a yankin. A wani sako da ya wallafa a dandalin X, Larijani ya zargi Firaministan IsraelBenjamin Netanyahu da rinjayar shugaban Amurka Donald Trump domin jefa Amurka cikin yaki da Iran.
Sai dai ma’aikatar tsaron Amurka, Pentagon, ta ce sojojin Amurka shida ne kawai suka mutu tun bayan fara rikicin, inda hudu daga cikinsu suka mutu a Kuwait. Larijani ya kuma yi gargadin cewa Iran za ta dauki fansa kan kisan jagoran addinin kasar Ali Khamenei, wanda aka kashe a hare-haren hadin gwiwa da Amurka da Isra’ila suka kai.
Rikicin ya kara tsananta a yankin Gabas ta Tsakiya bayan Iran ta fara kai hare-haren makamai masu linzami da jirage marasa matuki kan Isra’ila da sansanonin sojin Amurka. Hukumomin Iran sun ce suna shirye su ci gaba da yakin na dogon lokaci, tare da yin watsi da yiwuwar komawa tattaunawa da Amurka.














