Shugaban ƙasar Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, da takwaransa na Faransa, Emmanuel Macron, sun yi wata tattaunawa ta waya inda suka mayar da hankali kan yadda za a ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro tsakanin ƙasashen kawancen NATO. Hakan ya fito ne daga wata sanarwa da Hukumar Sadarwa ta Turkiyya ta fitar.
A yayin tattaunawar, shugabannin biyu sun kuma tattauna dangantakar da ke tsakanin ƙasashensu tare da musayar ra’ayi kan rikice-rikicen yankuna da na duniya da ke gudana a halin yanzu.
Erdogan ya jaddada cewa yanayin siyasar duniya a yanzu na nuna muhimmancin ƙara haɗin kai a fannin tsaro tsakanin ƙasashen NATO. Ya kuma yi kira da a hanzarta aiwatar da wasu shirye-shiryen haɗin gwiwar masana’antar tsaro da aka daɗe ana jinkirta su.
Haka kuma ya yi gargadin cewa tsawaita rikicin da ya shafi Iran na iya haifar da ƙarin rashin zaman lafiya a yankin, yana mai jaddada cewa Turkiyya na ci gaba da ƙoƙarin karfafa hanyoyin diflomasiyya da komawa kan teburin tattaunawa.














