Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta sanar cewa adadin mutanen da suka mutu sakamakon hare-haren Isra’ila tun daga watan Oktoba na 2023 ya kai 72,133, yayin da 171,826 suka jikkata. Rahoton ya nuna cewa duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da aka ayyana a Oktoba 2025, hare-haren Isra’ila na ci gaba a yankin.
A cikin awanni 24 da suka gabata kadai, an kai gawar mutane 7 da raunana 17 zuwa asibitoci a Gaza. Hukumomin lafiya sun ce tun bayan fara tsagaita wuta a ranar 10 ga Oktoba 2025, mutane 648 sun mutu yayin da 1,728 suka jikkatasakamakon hare-haren.
Haka kuma jami’an ceto sun ce an fitar da gawar mutane 755 daga karkashin baraguzai, yayin da ake zaton har yanzu gawarwaki da dama na nan a karkashin gine-ginen da suka rushe a fadin Gaza.














