Nijeriya

Taron gwamnoni a Legas ne ya hana ni zuwa Bikin Hawan Nasarawa – Gwamnan Kano

Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ƙaryata jita-jitar da ake yaɗawa cewa ya yi watsi da Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ta hanyar ƙin halartar Bikin Hawan Nasarawa da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar.

Newstimehub

Newstimehub

23 Mar, 2026

63fe8a339e86a1f3c5a1a84f3c2b20777ca58f57ef20995a2ee1c315a9997317 main

Gwamnatin Kano ta musanta rahotannin da ke yawo a wasu kafafen sada zumunta da ke zargin cewa gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, ya yi watsi da Sarki Muhammadu Sanusi II yayin bikin Hawan Nasarawa da aka gudanar a Gidan Gwamnatin Kano.

Gwamnatin ta bayyana rahoton a matsayin ƙarya tsagwaronta, mai cike da ruɗani kuma mara tushe. Ta ce an ƙirƙiro labarin ne da nufin yaudarar jama’a da kuma haddasa rashin jituwa a tsakanin al’umma.

A sanarwar da mai Magana da yawun gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Litinin,  ya jaddada cewa babu wani abu na raini ko wulakanci da aka yi wa Sarkin Kano.

A cewar sanarwar, rashin halartar Gwamna Yusuf a taron Hawan Nasarawa ta samo asali ne sakamakon bikin ya ci karo da wasu abubuwa da suka taso musamman taron gwamnonin Nijeriya wanda aka shirya gudanarwa a Legas wanda ake buƙatar halartarsa.

Duk da rashin halartar sa, an bayyana cewa Gwamna Yusuf ya bi dukkan ƙa’idoji ta hanyar sanar da Sarkin na Kano tun da wuri. Haka kuma ya ba da umarni ga manyan jami’an gwamnati su wakilce shi.

Daga cikin waɗanda suka wakilci gwamnan akwai Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano da sauran manyan jami’an gwamnati, waɗanda suka karɓi Sarkin na Kano a madadin gwamnan a Gidan Gwamnati.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa gwamnan ya halarci wasu muhimman bukukuwan Sallah. Ya yi sallar Idi da Sarkin Kano ya jagoranta, sannan ya halarci Hawan Daushe da aka gudanar a masarautar Gaya.

Bugu da ƙari, gwamnan ya shirya karɓar sarakunan Rano da Karaye da kuma Gaya da kansa, wanda ke nuna girmamawarsa ga sarakunan gargajiya.

Gwamnatin Jihar Kano ta sake jaddada cewa babu wata matsala ko rashin fahimta tsakanin gwamnati da Masarautar Kano. Ta ce dangantakarsu na nan daram bisa mutunta juna da kuma haɗin kai domin tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban jihar.