Gabas Ta Tsakiya

Amurka ta kai wa Iran sabbin hare-hare, in ji CENTCOM

Rundunar sojin Amurka ta ce hare-haren, waɗanda su irinsu na farko da ta kai kai tsaye kan Iran bayan dakatarwa na tsawon wasu kwanaki ‘‘martani ne mai karfi’’ ga yunƙurin Tehran na kai hari kan sojojin Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya.

Newstimehub

Newstimehub

30 Jul, 2026

1e0ef571 c516 4318 886c 0107ceef3260 1785372846119

Rundunar sojin Amurka ta ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Iran a matsayin martani ga “yunƙurin kai hare-haren Iran” kan sojojin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya, a cewar rundunar sojin Amurka CENTCOM).

Rundunar ta ƙara da cewa ta kai hari kan wasu cibiyoyin rundunar kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) ta Iran da safiyar ranar Alhamis bayan abin da ta bayyana a matsayin yunƙurin kai hare-haren makamai masu linzami kan sojojin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, rundunar CENTCOM ta ce dakarunta sun kai hari kan cibiyoyin bayar da umarnin sojoji da ma’ajiyar makamai masu linzami da na jiragen sama marasa matuƙa da wuraren sa ido da tsaron bakin teku da kuma tashar jiragen ruwa a faɗin Iran.

Ta ƙara da cewa, an kai hare-haren ne don rage barazanar da Iran da aƙwayenta ke yi wa sojojin Amurka da jiragen ruwa na kasuwanci da kuma ƙasashen yankin Gulf da ke maƙotaka da ita.

An ƙaddamar da sabbin hare-haren ne bayan da IRGC ta harba makamai masu linzami da dama daga Iran a ranar 28 ga Yuli, yanayin da ta kira yunƙurin kai hari na ba-zato-ba-tsammani kan sojojin Amurka da ke yankin, in ji rundunar sojin Amurka.

CENTCOM ta bayyana cewa an jibge sojojin Amurka fiye 50,000 a faɗin yankin Gabas ta Tsakiya kuma suna cikin shirin ko-ta-kwana yayin da tashin hankali ke ci gaba da ƙaruwa bayan musayar wuta ta baya bayan nan.

Kafafen yaɗa labaran gwamnatin Iran sun ba da rahoton fashewar abubuwa da dama a kudancin ƙasar, inda aka ji ƙarar fashewar abubuwa a birnin Bandar Abbas mai tashar jiragen ruwa da kuma ƙarin hare-hare a Tsibirin Qeshm.

A ‘yan makonnin nan, tashin hankali tsakanin Amurka da Iran ya ƙaru sosai, inda Washington ta kai hare-hare kan Iran, ita kuma Tehran ta mayar da martani ta hanyar kai hari kan cibiyoyin soji da muhimman wuraren Amurka a ƙasashe daban-daban na yankin.

“Tana kai musu hari da ƙarfi”

Hare-haren baya-bayan nan sun zo ne sa’o’i bayan da wani jirgin sama mara matuki ya kai hari kan wani jirgin ruwan dakon iskar gas (LNG) mallakin Amurka a Masar.

A farkon wannan rana, Trump ya ce sojojin Amurka za su kai wa Iran hari da ƙarfi bayan wani harin makami mai linzami kan sansanonin Amurka da ke Jordan, kamar yadda kafar Fox News ta rawaito.

“Za mu yi kai musu hari da ƙarfi. Za mu ragargaza su,” in ji wakilin Fox, yana mai ambaton Trump yana faɗa a ranar Laraba, ya kuma ƙara da cewa shugaban Amurka ya yi amfani da kalmomin zagi don jaddada matsayarsa: “Za mu karya ‘ƙarfin’ su.”

Trump ya kuma shaida wa Fox cewa harin bam da Amurka da Saudiyya suka kai wa ‘yan bindiga masu goyon bayan Iran a cikin dare a Iraki ya samu haɗin kai daga hukumomi a Baghdad, duk da cewa gwamnatin Iraki ta fito fili ta yi Allah wadai da hare-haren.

Trump “ya ce an haɗa kai da gwamnatin Iraki wajen kai waɗannan hare-hare,” kamar yadda wakilin Fox ya bayyana bayan ya yi zanta da shugaban Amurka.