Ofishin Babban Hafsan Sojojin Iran ya fitar da umarnin kare kai ba tare da kai hari ba a faɗin ƙasar, wanda ke bayyana shirye-shiryen da za a yi dangane da yanayi uku da ka iya faruwa: cikakken yaƙi da tsagaita wuta, da kuma kawo ƙarshen rikicin, kamar yadda kafar watsa labarai ta gwamnati ta bayyana a ranar Talata.
A cewar Kamfanin Dillancin Labarai na Fars, Manjo Janar Ali Abdollahi—wanda shi ne Babban Hafsan hafsoshin Sojojin Iran kuma shugaban Kwamitin Dindindin na Tsarin Kare Kai Ba Tare da Kai Hari Ba—shi ne ya fitar da wannan umarni da ya ƙunshi sassa 10 domin shirye-shiryen bikin tunawa da tsarin kare kai na ƙasar Iran na shekarar 2026.
Matakai daban-daban a yanayi daban-daban
A ƙarƙashin yanayin yaƙi, za a dakatar da manyan tarurrukan jama’a da kuma tarurrukan kai-tsaye, maimakon haka ayyukan za su mayar da hankali kan shirye-shiryen aiki da kiyaye muhimman kayayyaki da kula da albarkatun ƙasa da taimaka wa jama’a da kuma daidaita tsakanin hukumomin da abin ya shafa.
Idan aka cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta ba tare da kawo ƙarshen tashin hankali na dindindin ba, umarnin ya fi mayar da hankali kan shirye-shiryen jama’a da yin taka-tsantsan da kuma tsaron bayanai.
A ƙarƙashin yanayin kawo ƙarshen yaƙi, hukumomi za su aiwatar da atisayen da aka tsara da shirye-shiryen horaswa da ayyukan jama’a gaba ɗaya.
Umarnin ya kuma yi kira da a sabunta tsare-tsaren aiki bisa ga darussan da Iran ta bayyana a matsayin “yaƙe-yaƙe na biyu da na uku da aka ƙaƙaba.”
An bayar da umarnin a yayin da Amurka da Isra’ila ke ci gaba da yaƙar Iran
Iran ta fitar da irin wannan umarni mai sassa 10 ga shirye-shiryen tunawa da tsaron da ba a saba gani ba na shekara-shekara a 2024 da 2025, inda ta mayar da hankali kan shirye-shiryen jama’a da kuma kare muhimman kayayyakin more rayuwa.
Sabon umarnin ya bambanta ta hanyar yin shiri kai-tsaye don fuskantar ɗaya daga cikin sakamako guda uku da za a iya samu a yayin yaƙin da Amurka da Isra’ila ke yi da Iran.
Amurka da Isra’ila sun kai manyan hare-hare kan Iran a ranar 28 ga Fabrairu, inda suka kai hari kan gine-ginen gwamnati, cibiyoyin soji, ma’ajiyar makamai masu linzami da kuma garkuwar makamai masu linzami. Iran ta mayar da martani da hare-haren makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuki kan Isra’ila da sansanonin Amurka a duk fadin yankin.
Rikicin ya bazu a yankin tun lokacin da aka ci gaba da kokarin diflomasiyya na neman kawo karshen rikicin.
Kafin yakin da ake yi a yanzu, Iran da Isra’ila sun yi fada na tsawon kwanaki 12 a watan Yunin 2025 wanda ya ƙare da tsagaita wutar da Amurka ta shiga tsakani don cim mawa

















