Ƙara tsanantar faɗa tsakanin dakarun gwamnatin Yemen da ƙungiyar Houthi ya tilasta wa fiye da mutane 100,000 barin gidajensu a cikin ƙasar, yayin da wasu dubban mutane suka tsere zuwa ƙasashen waje, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya.
Dubban mutane sun tsere daga gidajensu sakamakon hare-haren da Houthi ta shafe mako guda tana kaiwa, waɗanda suka ƙare da ƙungiyar ta kwace ragowar gabar tekun Bahar Maliya ta Yemen tare da ƙara ƙarfafa ikonta kan Mashigar Bab al-Mandab.
Mashigar ta ƙara zama mai muhimmanci yayin da yaƙin Amurka da Iran ke kawo cikas ga zirga-zirgar jiragen ruwa ta Mashigar Hormuz.
Hukumar kula da ’yan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNHCR) ta yi gargadi a cikin wata sanarwa a ranar Talata cewa:
“Ƙara tsanantar tashin hankali cikin sauri a gabar tekun yammacin Yemen ya raba sama da mutane 100,000 da muhallansu a cikin ƙasar, tare da tilasta wa wasu dubban mutane neman mafaka” a ƙasar Djibouti.
Hukumar ta ce fadan ya raba iyalai da muhallansu a wani faɗin yanki, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin cewa za a iya samun ƙarin gudun hijira a cikin Yemen da kuma ƙarin kwararar ’yan gudun hijira idan rikicin ya ƙara tsananta.
UNHCR ta ce fiye da mutane 2,400 sun tsallaka teku daga Yemen zuwa Djibouti cikin kwanaki huɗu kacal da suka gabata, inda mata, yara da tsofaffi suka kasance sama da kashi 60 cikin 100 na waɗanda suka isa.
Sandrine Desamours, wakiliyar UNHCR a Djibouti, ta ce:
“Mutane na isa bayan sun yi doguwar tafiyar teku mai wahala. Da yawa daga cikinsu sun gaji, sun shiga damuwa, kuma suna ɗauke da kaɗan daga cikin abubuwan da suka iya kwaso.”
“Taimakon da ake bayarwa ya riga ya shiga matsala. Muna matuƙar buƙatar ƙarin tallafi cikin gaggawa kafin ƙarin iyalai su iso.”
UNHCR ta ce iyalan da suka rasa matsugunansu a cikin Yemen sun tsere cikin gaggawa, ba tare da sun samu damar kwashe kayayyaki da yawa ba. Wannan ya ƙara nuna buƙatar samar da matsuguni, abinci, ruwan sha mai tsafta, kiwon lafiya da ayyukan kariya.
Hukumar ta kuma bayyana damuwa kan ƙarin haɗarin da sama da ’yan gudun hijira da masu neman mafaka 65,000 da aka yi wa rajista a Yemen ke fuskanta, galibinsu daga Somaliya da Habasha.
Ta ce samun damar kai agajin jinƙai ga waɗanda abin ya shafa na ci gaba da kasancewa babban ƙalubale.
A cewar hukumar:
“Rashin tsaro, lalacewar hanyoyi, katsewar hanyoyin sadarwa da takaita zirga-zirga na kawo cikas ga ayyukanmu.”
Ƙara tsanantar rikicin ta kuma haifar da damuwa game da tasirinsa kan jigilar kayayyakin agajin jinƙai a duniya, wadda tuni ke fuskantar matsin lamba sakamakon ci gaba da samun cikas a yankin Mashigar Hormuz.
UNHCR ta ce ci gaba da rashin tsaro a kusa da Mashigar Bab al-Mandab, wadda muhimmiyar hanyar sufuri ce ta teku da ta haɗa Bahar Maliya da Tekun Aden, na iya shafar jigilar kayayyakin agaji da na kasuwanci zuwa Yemen, Sudan da sauran wuraren da ake fama da matsalolin jinƙai a yankin da ma wajensa.















