Afirka Wasanni

CAF ta sanar: Za a rika shirya Gasar AFCON duk bayan shekara huɗu daga 2028

CAF ta yanke shawarar sauya tsarin gudanar da AFCON daga duk bayan shekara biyu zuwa duk bayan shekara huɗu, domin daidaita jadawalin ƙwallon ƙafar Afirka da na duniya tare da ƙara hanyoyin samun kuɗi.

Newstimehub

Newstimehub

22 Dec, 2025

d25049f00ac71bc499732a8776e4050871fab70af8fb903f422a3c68a6258355 e1766391127253

Patrice Motsepe shugaban hukumar kula da harkokin ƙwallon ƙafa ta Afirka (CAF),  , ya bayyana a ranar Asabar cewa daga shekarar 2028 za a riƙa gudanar da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka (AFCON) duk bayan shekara huɗu-huɗu.

Motsepe ya ce wannan mataki na daga cikin manyan sauye-sauyen da CAF ke shirin kawowa a harkar ƙwallon ƙafar Afirka, domin a daidaita jadawalin gasar da tsarin ƙwallon ƙafa na duniya. Ya bayyana cewa duk da cewa shirya gasar AFCON bayan shekaru biyu-biyu na samar wa ƙungiyoyin Afirka kuɗin shiga, CAF na da burin ƙaddamar da gasar lig ta ƙasashen Afirka, wadda za ta yi kama da gasar UEFA, domin ƙara wa ƙasashen kudaden shiga.

“Babban abin da ke gabanmu a yanzu shi ne gasar AFCON, amma daga shekarar 2027 za mu je Tanzania, Kenya da Uganda, sannan gasar AFCON ta gaba ita ce wadda za a gudanar a 2028,” in ji Motsepe yayin wata ganawa da manema labarai a birnin Rabat na ƙasar Maroko, a daidai lokacin da ake shirin soma AFCON 2025.

Damar ɗaukar nauyin gasar

Motsepe ya kuma bayyana cewa CAF za ta bai wa ƙasashen da ke sha’awa damar neman ɗaukar baƙuncin Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka ta 2028. “Bayan Gasar Cin Kofin Duniya ta Ƙungiyoyin Ƙwallon Ƙafa ta FIFA a 2029, za mu ƙaddamar da gasar lig ta ƙasashen Afirka ta farko, inda za a zuba ƙarin kuɗaɗe, kayan aiki da gasa mai ƙarfi. “A matsayin wani ɓangare na wannan tsari, za a riƙa gudanar da gasar AFCON duk bayan shekara huɗu-huɗu,” in ji shi.

Majıyar Labari: Trt Hausa