Ministan Harkokin Wajen Koriya ta Kudu, Cho Hyun, ya ce Seoul da Washington suna tattaunawa kan yiwuwar ɗauke wasu daga cikin na’urorin kariyar makami mai linzami ta Patriot da ke Koriya ta Kudu, bayan rahotannin da ke cewa za a iya mayar da su Gabas ta Tsakiya don tallafawa yaƙi da Iran.
A yayin wani zama na sauraron shaida a majalisa a ranar Juma’a, Cho ya ce hukumomin soja na ƙasashen biyu suna tattaunawa sosai, amma ya ƙi tabbatar da ko za a miƙa makaman ba da jimawa ba don amfani da su a rikicin da ya shafi Iran.
“Gabaɗaya, hukumomin soja na ƙasashen biyu suna ci gaba da tattaunawa sosai game da tura kadarorin,” in ji Cho, yana ƙarawa da cewa ba zai iya yin tsokaci kai tsaye kan yiwuwar sauyin ba.
Maganganun sun biyo bayan rahotannin kafafen watsa labarai na Koriya ta Kudu masu cewa an kwashe wasu na’urorin na tare makamai, samfurin Patriot daga wasu sansanonin Amurka a cikin ƙasar zuwa Filin Jirgin Sama na Osan a Pyeongtaek, lardin Gyeonggi. Rahotannin sun ambato majiyoyin gwamnati na cewa ta yiwu ana shirin tura waɗannan na’urorin zuwa Gabas ta Tsakiya.
An kuma ga jiragen saman jigilar soja na Amurka, ciki har da C-17 da C-5, suna isa wannan filin, a cewar rahotannin cikin gida, abin da ya ƙara haifar da zato cewa za a iya ɗauke na’urorin daga Koriya ta Kudu.
A bara, an mayar da rukuni biyu na Patriot zuwa Gabas ta Tsakiya a jirgin C-17, watanni kaɗan kafin Amurka da Isra’ila su kai hari kan wuraren makamashin nukiliyar Iran a watan Yuni. An mayar da waɗannan na’urorin na Patriot zuwa Koriya a watan Oktoba.
Wannan labarin ya fito ne a daidai lokacin da ake samun rahotannin cewa jami’an Turai sun nuna damuwa kan ƙarancin makaman dakatarwar, yayin da rikice-rikicen Gabas ta Tsakiya da Ukraine ke ci gaba.
Jami’an sojin Amurka a Korea sun ƙi yin tsokaci kan waɗannan rahotanni.
“Saboda dalilan tsaro na aikin soja, ba ma yin tsokaci kan safara, mayarwa ko yiwuwar sake wurin wasu kayan soja ko kadarori na musamman,” in ji rundunar a cikin wata sanarwa.
Cho ya ce Koriya ta Kudu ba ta karɓi kowace buƙata ta hukuma daga Washington ba don tallafin kayan soja da ya shafi rikicin ba.
A baya, Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Washington za ta karɓi taimako daga kowace ƙasa kan yaƙin da suke yi kan Iran.
Wannan ya zo ne yayin da sojojin Amurka da na Isra’ila suka kai hare-hare kan muhimman wurare a cikin Iran tsawon kwanaki da dama a jere, abin da Trump ya bayyana a matsayin yunƙurin raunana ikon Tehran na ƙera makaman nukiliya da masu linzami da dogon zango.
Koriya ta Kudu na ɗauke da kusan sojojin Amurka 28,500 a matsayin wani ɓangare na haɗin gwiwar kariya na ƙawance kan barazanar Koriya ta Arewa mai makamin nukiliya, tare da samun tsarin kariyar sama da yawa a yankin, ciki har da na’urorin dakatar da makamai ta Patriot.














