An samu ɗan ƙaramin sauƙi a ƙasar Nigeria bayan sakin wasu daga cikin daliban makarantar Katolika ta St. Mary’s Papiri da aka sace ranar 21 ga Nuwamba. A lokacin sace-sacen, fiye da dalibai 300 da malamai 12 aka yi garkuwa da su. Duk da haka, sama da yara 150 har yanzu na ci gaba da kasancewa a hannun masu garkuwa.
Wakiliyar UNICEF Nigeria ta bayyana damuwa kan lafiyar yaran da aka saki, inda ta ce bayan tsawon lokacin da suka shafe a cikin tsoro da wahala, suna bukatar cikakken duba na likitoci. Hukumomi sun bayyana sakin na farko a matsayin nasara, suna roƙon jama’a da su ci gaba da addu’a domin kubutar da sauran yaran.
Ko da yake babu ƙungiya da ta ɗauki alhakin wannan aika-aika, mazauna yankin na zargin ‘yan fashi masu garkuwa da mutane da ke kai hare-hare domin karɓar kuɗin fansa. Masana na ganin cewa yawan biyan fansa a ɓoye ke sa hukumomi su ci gaba da yin shiru kan ayyukan ceto.
Asil: Africa News














