Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (CAF) ta yi kakkausar suka kan abin da ta kira “halayen da ba su dace ba” da wasu ‘yan wasa da jami’ai suka nuna a wasannin kwata-final na gasar AFCON Morocco 2025, tare da buɗe bincike na hukuma kan abubuwan da suka faru.
CAF ta ce bayan duba rahotannin alkalai da faifan bidiyo, ta gano yiwuwar aikata laifuffuka a wasannin da suka haɗa Kamaru da Morocco, da kuma Algeria da Nijeriya. Wasan Morocco da Kamaru, wanda masu masaukin baki suka ci 3–2, ya rikide zuwa rikici bayan tashi, inda ‘yan wasa suka yi musayar zafafan kalamai har jami’an tsaro suka shiga tsakani.
A daya bangaren kuma, nasarar Nijeriya da ci 2–0 a kan Algeria ta jawo fushin ‘yan Algeria, inda suka zargi alkalai da son kai, musamman kan ƙin ba su bugun fenariti. Rikici ya ɓarke bayan wasan, har sai da jami’an tsaro suka kewaye alkalin wasa da tawagarsa domin kare su.
CAF ta ce ta tura dukkan lamurran zuwa Hukumar Ladabtarwa domin cikakken bincike, tana mai jaddada cewa za a ɗauki mataki kan duk wanda aka samu da laifi. Hukumar ta kuma sake nanata cewa ba za ta lamunci duk wani rashin ladabi ko cin mutuncin alkalai da jami’an gasar ba.













