Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Senegal ta tsallaka zuwa wasan kusa da na ƙarshe a gasar cin kofin Afrika ta 2025 (CAN), bayan ta doke Mali da ci 1-0 a wasan kwata fainal da aka buga a filin wasa na Ibn-Batouta da ke Tangier, Morocco.
Ɗan wasan Senegal, Iliman Ndiaye ne ya zura ƙwallon da ta ba ƙasarsa nasara a minti na 28, bayan kuskuren da mai tsaron ragar Mali, Djigui Diarra, ya yi.
Mali ta rage da ’yan wasa goma bayan korar Yves Bissouma a ƙarshen rabin farko, amma duk da haka ta tsaya kai da fata a kashi na biyu, tana hana Senegal ƙara ci.
Senegal, wadda ake ɗauka a matsayin ɗaya daga cikin manyan ’yan takarar lashe kofin, za ta fafata a wasan kusa da na ƙarshe da wanda ya yi nasara tsakanin Masar da Côte d’Ivoire.














