An Ji Kararrawar Gaggawa a Bahrain Bayan Hare-haren Iran

An kunna kararrawar gaggawa a Bahrain yayin da hukumomi suka bukaci jama’a su nemi mafaka bayan hare-haren ramuwar gayya da Iran ke kaiwa a yankin.
4 Mar, 2026
MDD(United Nation) Ta Nuna Fargaba Kan Sabbin Rikice-Rikice Bayan Hare-haren Amurka da Isra’ila

Majalisar Dinkin Duniya ta nuna damuwa kan karuwar rikicin Gabas ta Tsakiya bayan hare-haren Amurka da Isra’ila kan Iran da kuma yiwuwar tasirinsa ga fararen hula da tattalin arzikin duniya.
4 Mar, 2026
Iran Ta Ce Babu Batun Tattaunawa Da Amurka Yayin Da Rikici Ke Ci Gaba

Iran ta ce babu wani shiri na tattaunawa da Amurka a yanzu yayin da rikicin da ya biyo bayan hare-haren Amurka da Isra’ila kan Tehran ke ci gaba.
3 Mar, 2026
Rikicin Gabas Ta Tsakiya Na Haddasa Fargaba Ga Masu Tafiya Umara

Rikicin da ke gudana tsakanin Amurka, Isra’ila da Iran ya haddasa katsewar wasu tafiye-tafiyen jiragen sama, lamarin da ke jefa masu tafiya Umara daga Nijeriya cikin fargaba da rashin tabbas.
3 Mar, 2026

Hezbollah Ta Kai Hare-Hare Kan Sansanonin Sojin Isra’ila Da Rokoki Da Jiragen Drone

Iran Ta Ce Ta Kai Hare-Haren Ramuwar Gayya Kan Wurare 500 Masu Alaƙa Da Isra’ila Da Amurka

Sabbin Fashewar Bam A Tehran Bayan Isra’ila Ta Kaddamar Da Sabuwar Farmaki

Ƙasashen Afirka Sun Ɗauki Matakan Gaggawa Domin Kare ’Yan Ƙasarsu Yayin Rikicin Gabas Ta Tsakiya

Jiragen yaƙin Amurka da dama sun faɗi a Kuwait, in ji ma’aikatan tsaron Kuwait
2 Mar, 2026
Faransa Ta Ce Harin Kan Iran a Wajen Kwamitin Tsaro na MDD “Abin Takaici Ne”
Faransa ta bayyana farmakin kan Iran a wajen Kwamitin Tsaro na MDD a matsayin abin takaici, tana kira da a dakatar da rikicin tare da neman mafita ta siyasa.

2 Mar, 2026
Adadin Mace-Mace Ya Kai 555 a Hare-Haren Amurka da Isra’ila Kan Iran
Ƙungiyar Iranian Red Crescent ta ce mutane 555 sun mutu a hare-haren Amurka da Isra’ila kan Iran, yayin da rikicin ke ci gaba da tsananta.

2 Mar, 2026
Saudiyya Ta Dakile Hare-Haren Jiragen Sama Marasa Matuki Kan Matatar Mai ta Ras Tanura
Saudiyya ta ce ta tare jiragen sama marasa matuki biyu da suka yi yunƙurin kai hari kan matatar mai ta Ras Tanura, ba tare da an samu asarar rayuka ba.

2 Mar, 2026
Hare-Haren Iran Sun Hallaka Mutane a Isra’ila, Rikici Na Ƙara Tsananta
Aƙalla mutum 12 sun mutu a Isra’ila bayan Iran ta ƙara yawan hare-haren makamai masu linzami, duk da matakan kariya na sararin samaniya.

2 Mar, 2026
Isra’ila Ta Kaddamar da Sabon Farmaki Kan Lebanon, Za a Shafe Kwanaki Ana Kai Hare-Hare
Isra’ila ta fara wani farmaki na kwanaki da dama kan Lebanon bayan hare-haren makamai da Hezbollah ta kai zuwa Haifa.

1 Mar, 2026
Iran ta kafa majalisar jagorancin wucin-gadi a Iran bayan kashe Khamenei
Gidan talabijin na gwamnati a ƙasar a ranar Lahadi ya sanar da zaman makokin kwanaki 40 da kuma hutu na kwanaki bakwai ga jama’a bayan mutuwar babban jagoran ƙasar mai shekaru 86, wanda yake riƙe da madafun iko tun 1989.

1 Mar, 2026
Nijeriya, Senegal da Libya Sun Nemi Tsagaita Wuta a Rikicin Isra’ila-Amurka da Iran
Ƙasashe da ƙungiyoyi na duniya sun nuna damuwa kan ƙarin tashin hankali tsakanin Iran, Isra’ila da Amurka, suna kira ga tsagaita wuta da komawa diflomasiyya.

1 Mar, 2026
Iraniyawa suna zanga-zanga bayan Amurka da Isra’ila sun kashe Khamenei
Iraniyawa sun fantsama kan tituna inda suke gudanar da zanga-zanga tare da yin alini bayan Amurka da Isra’ila sun kashe Jagoran Addini na ƙasar Khamenei a harin da suka kai masa.

1 Mar, 2026
Gwamnatin Iran ta tabbatar da kisan Ali Khamenei da iyalansa
Tehran ta sanar da mutuwar Jagoran Addini Ayatollah Ali Khamenei tare da ayyana makoki da kuma alwashin ramuwar gayya daga rundunar juyin-juya-hali.

1 Mar, 2026
Iran ta musanta iƙirarin Amurka da Isra’ila na kashe Jagoran Addini Ali Khamenei
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta yi watsi da iƙirarin Netanyahu da Trump, tana mai cewa Shugaban Addini na Iran Khamenei da shugaban ƙasar Pezeshkian suna “cikin aminci da ƙoashin lafiya”.

