Ghana da Zambia sun ɗauki wani muhimmin mataki na ƙarfafa dangantaka bayan amincewa da tafiya ba tare da biza ba tsakanin ‘yan ƙasashen biyu. Wannan mataki ya zo ne a yayin ziyarar aiki ta kwana uku da Shugaban Ghana, John Dramani Mahama, ya kai Zambia, domin bunƙasa alaƙar siyasa, tattalin arziki da mu’amala tsakanin al’ummomin ƙasashen biyu.
Ministan harkokin wajen Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa, ya bayyana cewa ɗauke buƙatar bizar na daga cikin manyan nasarorin ziyarar, yana mai cewa zai sauƙaƙa tafiye-tafiye tare da buɗe ƙofofi ga kasuwanci, yawon buɗe ido, zuba jari da musayar al’adu. Shugaba Mahama ya isa Lusaka ranar Laraba, 4 ga Fabrairu, inda takwaransa Shugaba Hakainde Hichilema ya tarbe shi a filin jirgin saman Kenneth Kaunda.
A cewar Mista Ablakwa, wannan shi ne karo na farko a tarihin dangantakar Ghana da Zambia da aka cim ma tafiya babu biza, matakin da ake sa ran zai rage cikas ga ɗalibai, ‘yan kasuwa, masu yawon buɗe ido da ƙwararru, tare da ƙarfafa haɗin kai tsakanin ƙasashen biyu.
Majiyar Labari: TRT HAUSA














