Kungiyar Haɗin Kan Musulmi, Organisation of Islamic Cooperation, ta sanar da shirya taron gaggawa na ministocin harkokin waje a Jeddah domin tattauna matakan Israel na faɗaɗa matsuganan ‘yan-kama-wuri-zauna da kuma batun haɗa West Bank cikin ƙasarta. An ce Falasdinu ne ya nemi taron domin daidaita matsayi da tattauna yiwuwar ɗaukar mataki.
Sanarwar OIC ta bayyana damuwa cewa sabbin shawarwarin Isra’ila na iya sauya matsayin doka da siyasa na yankin, tare da kawo cikas ga mafarkin samar da tsarin kasashe biyu. Wannan na zuwa ne bayan rahotannin cewa Isra’ila ta amince da rajistar wasu yankuna a matsayin mallakin ƙasa.
Kafafen yada labarai na Isra’ila sun ce matakin ya haɗa da canje-canje a dokokin rajistar ƙasa. A gefe guda, Falasdinawa sun yi gargadin cewa irin waɗannan matakai na iya rage yiwuwar kafa ƙasar Falasdinu mai zaman kanta.
Rikicin na ci gaba da janyo muhawara a matakin ƙasa da ƙasa, yayin da ƙungiyoyi da kasashe ke bibiyar halin da ake ciki a yankunan Falasdinu.














