A cewar Ma’aikatar Harkokin Waje ta Saudiyya, Bin Farhan ya yi magana ta waya da Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, inda suka tattauna hanyoyin ƙarfafa tsaro da kwanciyar hankali. Haka nan ya tattauna da Ministan Harkokin Wajen Oman, Badr Albusaidi, da kuma Firaministan Qatar, Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al Thani, kan muhimmancin diflomasiyya wajen hana tashin hankali.
Tattaunawar ta zo ne bayan Shugaban Amurka Donald Trump ya sassauta kalamai kan Iran, duk da gargadin da ya yi game da yiwuwar ɗaukar mataki idan lamarin ya ƙara tsananta.
Tsoron yiwuwar harin Amurka kan Iran ya ƙaru ne sakamakon zanga-zangar da ke gudana a ƙasar da kuma rahotannin Isra’ila na cewa ana iya kai hari nan gaba kaɗan.














