Akalla masu haƙar ma’adinai 38 ne suka mutu, yayin da wasu 27 suka jikkata sakamakon fashewar tukunyar gas a wani wurin haƙar ma’adinai a jihar Filato. Majiyoyin yankin sun ce hatsarin ya faru ne a mahaƙar Zurak da ke gundumar Bashar.
Muƙaddashin sarkin gargajiya na yankin, Aliyu Adamu Idris, ya tabbatar da adadin mamatan, yana mai cewa an garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibiti. Shaidu sun bayyana cewa fashewar ta faru ne da safe yayin da ma’aikata ke karkashin ƙasa.
Wani ma’aikacin haƙar ma’adinai da ke kusa da wurin ya ce an yi ƙoƙarin ceto mutanen, amma da yawa sun rasa rayukansu. Rahoton tsaro da aka gani ya danganta mutuwar da shaƙar gubar carbon monoxide.
Jihar Filato, wadda aka daɗe ana sani da ayyukan haƙar ma’adinai, ta sha fama da irin waɗannan hatsarori. Hukumomi sun dade suna nuna damuwa kan matsalolin tsaro da ke da nasaba da haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba.
Majiyar Labari: TRT HAUSA














