Afirka

Nijar na zargin Faransa da tunzura sojojin da suka yi yunkurin tawayen da aka dakile

Gwamnatin Nijar ta gudanar da taron Majalisar Ministoci a ranar Jumma’a, wanda shi ne karo na farko tun bayan yunƙurin tawayen da wasu sojoji suka yi a ƙasar inda gwamnatin ta bayyana waɗanda take zargi suna da hannu a shirin tawayen.

Newstimehub

Newstimehub

5 Sep, 2026

2194fd42 c825 4690 a211 c5fcb9964efe 1788595519444

Gwamnatin Nijar ta zargi Faransa da tunzura wani hari da sojojin da suka yi yunƙurin tawaye suka kai a wani muhimmin sansanin sojin sama a babban birnin ƙasar, Yamai, a makon da ya gabata.

Gwamnatin ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin na ƙasar a ranar Jumma’a.

Sojojin da suka yi yunƙurin tawayen sun kai hari filin jirgin sama da fadar shugaban ƙasa a Yamai a ranar 29 ga Agusta, a wani sabon ƙalubale ga mulkin shugaban gwamnatin ƙasar, Abdourahamane Tiani.

An kuma ji fashewar abubuwa da ƙarar harbe-harbe a wani sansanin sojin sama da ke babban birnin. Sai dai sojojin Nijar, tare da taimakon sojojin haya na Rasha, sun sake karɓe iko da sansanin washegari.

Bayan taron Majalisar Ministoci a ranar Jumma’a, gwamnatin Nijar ta ce ta gano cewa wani babban gungu ne ya tunzura harin, wanda Faransa ke jagoranta.

Gwamnatin ta ce ta tattara dumbin shaidu da ke da alaƙa da harin, tare da gargadin cewa Nijar na da damar kai ƙarar lamarin gaban kotunan ƙasa da ƙasa.

Boren ya sake bayyana irin tashin hankalin da ke cikin rundunar sojin Nijar, wadda ta fuskanci asarar dakarunta sau da dama a fagen daga yayin da take yaƙi da ƙungiyoyin masu tsattsauran ra’ayin jihadi.

Gwamnatin sojin Nijar ta kuma sha zargin Faransa da wasu ƙasashen Afirka ta Yamma da hannu wajen tashe-tashen hankula da suka faru a babban birnin ƙasar a farkon wannan shekarar, amma ba ta gabatar da hujjojin da za su tabbatar da waɗannan zarge-zargen ba.