Nijeriya ta zo ta farko a duniya a tagomashin kasuwar hannun-jari

Nijeriya na cin moriyar haɓakar madafan tattalin arziƙi, sakamakon aiwatar da sauye-sauye da ƙaruwar farashin ɗanyen mai a duniya, da kuma haɓakar darajar kuɗi a kasuwar musaya.
10 Jul, 2026
Wasu da ake zargi ’yan ISWAP ne da iyalansu sun miƙa wuya ga sojojin Nijeriya

Abubuwan da aka ƙwato a hannun ’yanta’addan da iyalansu sun haɗa da jimillar kuɗi sama da Naira miliyan 1.5, wayoyin salula na Tecno guda biyu, da sauran kayayyaki.
9 Jul, 2026
Matatar mai ta Dangote ta fara dakon fetur kyauta zuwa wasu jihohin Nijeriya

A cewar kamfanin, wannan hidima ta sufurin mai kyauta ta shafi jihohin Legas da Ogun da Rivers da Kaduna da Delta da kuma Babban Birnin Tarayya, Abuja.
8 Jul, 2026
Majalisar Dattawan Nijeriya ta buƙaci a soke shirin gyaran hali na tubabbun ‘yan Boko Haram

Shirin gwamnatin Nijeriya na gyaran hali da kuma sake mayar da ‘yanta’adda da suka tuba cikin al’umma ya kasance ɗaya daga cikin manyan batutuwan da suka yi ta jawo ce-ce-ku-ce kan dabarun yaƙi da ta’addanci mafi rikitarwa a Nijeriya.
8 Jul, 2026

Jihar Legas ta kama mabarata 396, tana tantance bayanansu domin mayar da su jihohinsu na asali

Gwamnatin Nijeriya ta bai wa ‘yan ƙasarta damar ƙarshe ta kwashe su daga Afirka ta Kudu

‘Yansandan Nijeriya sun daƙile harin ‘yanbindiga a Sokoto, sun ƙwato AK-47

Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da fara ayyukan Bama zuwa Banki da Dikwa zuwa Gamboru-Ngala

Hukumar INEC ta Nijeriya ta tsawaita aikin rajistar masu zaɓe da makwanni biyu
4 Jul, 2026
Kotu ta samu mutum biyu da laifin ta’addanci a Nijeriya
Rundunar ‘yansandan ƙasar ta ce an fara sharia’r mai alaƙa da ta’adanci ne a jihar Katsina bayan an kama mutanen a wani babban samame kan safarar makamai a watan Satumbar 2025.

3 Jul, 2026
Nijeriya ta ƙaddamar da masana’antar sarrafa lithium mafi girma a Yammacin Afirka a jihar Nassarawa
Masana’antar, wacce Kamfanin Avatar New Energy Materials ya gina, ana sa ran za ta sarrafa ma’adinan lithium zuwa kayayyaki masu daraja don amfani da su a cikin batirin motocin lantarki da sauran fasahar makamashi mai tsabta.

3 Jul, 2026
Amurka ta janye akasarin sojojinta da ta aika Nijeriya
Kwamandan Rundunar Amurka ta Afrika (AFRICOM) ne ya sanar da batun janyewar a ranar Alhamis inda ya ce an janye dakarun ne tun bayan harin da aka kai a watan Mayu wanda ya kashe Abu-Bilal al-Minuki, mataimaki na biyu a jagorancin ƙungiyar Daesh.

2 Jul, 2026
Yunwa ta kai mummunan mataki da bai taɓa kai wa ba a shekaru 10 a Arewacin Nijeriya – WFP
Rikicin yana ƙara muni a lokacin damina, inda iyalai ke rasa abinci a rumbunansu kafin lokacin girbi.

2 Jul, 2026
Sojojin Nijeriya sun kashe ’yanta’adda 662, sun ceto 951 da aka sace cikin watanni uku
Hedkwatar Tsaron Nijeriyar ta ce dakarunta sun kashe ’yanta’adda 662 da sauran gungun masu laifi, sun kama mutane 1,084 da ake zargi, kuma sun ceto mutane 951 da aka yi garkuwa da su a faɗin ƙasar a zango na biyu na shekarar 2026.

1 Jul, 2026
CBN ya soke lasisin ƙananan bankuna na Microfinance 46 saboda rashin cika ƙa’idoji
CBN ya ce wannan mataki zai taimaka wajen tsaftace tsarin microfinance a Nijeriya tare da ƙarfafa bankunan da ke aiki bisa ƙa’ida da ƙarfi.

1 Jul, 2026
Nijeriya ta yi alƙawarin tallafa wa ‘yan ƙasar 271 da suka dawo daga Afirka ta Kudu
Ministan Harkokin Jinƙai da Rage Talauci, Dakta Bernard Doro ya ce gwamnati na ci gaba da jajircewa wajen kare mutunci da walwalar ‘yan Nijeriya a duk inda suke.

30 Jun, 2026
Gwamnatin Nijeriya ta karɓi ‘yan ƙasar 269 da aka sake mayarwa gida daga Afirka ta Kudu
Gidan taladijin ɗin ya ambato wata sanarwar daga ma’aikatar na cewa ambassada Ali-Gombe ya miƙa saƙon gaisuwar Shugaba Tinubu yana mai tabbatar da cewa gwamnati ta duƙufa ga kare ‘yan Nijeriya a ketare.

30 Jun, 2026
Jam’iyyar adawa ta NDC a Nijeriya ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin kotu game da rijistarta
Wannan na zuwa ne ‘yan kwanaki bayan wata babbar kotun tarayya a birnin Lokoja ta jihar Kogi, ta jingine hukuncin da ta yanke daga farko da ya bai wa hukumar zaɓe (INEC) umarnin yi wa NDC rijista a matsayin jam’iyyar siyasa.

29 Jun, 2026
‘Yanta’addan Boko Haram sun kai hari makaranta sun kashe malami tare da sace dalibai a Jihar Borno
Sun yi ta buɗe wuta , inda suka kashe malami ɗaya da kuma ji wa wasu mutane ciwo kafin su yi garkuwa da wasu ɗalibai da ba a san adadinsu ba



