Afirka

Sabon Rikici a Sudan ta Kudu Ya Raba Fiye da Mutane 180,000 da Gidajensu

Sabon rikici a jihar Jonglei ta Sudan ta Kudu ya tilasta wa fiye da mutane 180,000 barin gidajensu, yayin da artabu tsakanin dakarun gwamnati da na ‘yan adawa ke ƙara tsananta.

Newstimehub

Newstimehub

25 Jan, 2026

6fe50b92aedf62775579c825cee1dc6a328dcd84470de96a803a1c536466814f

Sabon tashin hankali da ya ɓarke a Sudan ta Kudu ya jefa dubban fararen hula cikin firgici, inda ake ci gaba da jin karar harbe-harbe da fashewar bama-bamai a wasu yankuna. Mutane na tserewa daga gidajensu zuwa dazuzzuka da wuraren da suka fi ganin aminci, domin tsira da rayukansu daga mummunan rikicin da ke ƙara tsananta.

A cewar rahotannin Majalisar Ɗinkin Duniya (OCHA), fiye da mutane 180,000 ne aka raba da muhallansu a jihohi huɗu na jihar Jonglei, bayan sabbin faɗace-faɗace tsakanin dakarun gwamnati da na ‘yan adawa. Shaidu sun ce an yi artabu mai tsanani a yankin Duk, inda aka yi amfani da manyan makamai, lamarin da ya tilasta wa al’umma tserewa zuwa kurmi.

Wani mazaunin yankin, Daniel Deng mai shekara 35, ya ce ya rasa komai sakamakon rikicin. “Ba ni da inda zan dosa sai daji, domin a can ne kawai na ke ganin rayuwa za ta fi aminci,” in ji shi.

Rikicin ya ƙara muni ne bayan da aka kama Mataimakin Shugaban Ƙasa Riek Machar a watan Maris, wanda ya janyo rikicewar yarjejeniyar raba madafun iko tsakaninsa da Shugaba Salva Kiir. Tun daga lokacin, artabu ya ƙara yawaita, musamman a watan Disamba a Jonglei.

Majiyar Labari: TRT HAUSA