Amurka Duniya

Trump Ya Ƙara Nijeriya da Ƙasashen Afirka 12 a Jerin Masu Biyan Kuɗin Ajiyar Biza Har $15,000

Amurka ta ƙara Nijeriya da ƙasashe 12 na Afirka cikin jerin ƙasashen da za a biya kuɗin ajiyar biza har zuwa $15,000 domin takaita karya ka’idar zaman biza.

Newstimehub

Newstimehub

7 Jan, 2026

acaa452a0c109b11ff053c88345039ee03a56790d066769cf3694db32ffa0d05

Gwamnatin Amurka ƙarƙashin Shugaba Donald Trump ta ƙara Nijeriya tare da ƙasashen Afirka 12 da wasu ƙasashe daga Latin Amurka da Asiya cikin jerin ƙasashen da za a tilasta wa ’yan ƙasarsu biyan kuɗin ajiyar karya ka’idar bizar zama a Amurka, wanda zai iya kaiwa daga dala $5,000 zuwa $15,000.

Wannan mataki ya biyo bayan ƙarin ƙasashe da aka saka a makon da ya gabata, inda yanzu jimillar ƙasashen da shirin ya shafa ta kai 38. Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta bayyana cewa sabbin ƙasashen da aka ƙara za su fara biyan kuɗin daga 21 ga Janairu, 2026.

Sabbin ƙasashen da wannan doka ta shafa sun haɗa da Algeria, Angola, Benin, Burundi, Côte d’Ivoire, Djibouti, Gabon, Uganda, Senegal, Togo, Zimbabwe, Venezuela da kuma Nijeriya, tare da sauran ƙasashen da ke cikin jerin tun farko. Matakin, a cewar hukumomin Amurka, na daga cikin ƙoƙarin ƙara tsaurara sharuɗɗan shiga ƙasar, domin tabbatar da cewa masu neman biza ba sa karya ka’idar tsawon lokacin da aka ba su. Duk da haka, an bayyana cewa kuɗin ajiyar za a mayar da shi idan aka hana mutum biza ko kuma idan mai bizar ya bi ka’idodi yadda ya dace.

Majiyar Labari: TRT HAUSA