Turkiyya na karɓar baƙuncin wani muhimmin taron tattaunawa kan alaƙarta da Afirka, wanda MIT ta shirya ƙarƙashin Shirin Tattaunawar Dabarun Turkiyya–Afirka. Taron na kwanaki biyu, daga 9 zuwa 10 ga Fabrairu, ana gudanar da shi a Ankara, tare da halartar manyan wakilai daga Turkiyya da ƙasashen Afirka da dama, ciki har da Somalia, Sudan, Kenya, Habasha, Eritireya, Nijeriya, Masar, Chadi, Afirka ta Kudu, Senegal da Gambiya.
Shirin ya haɗa da manyan jawabai da kwamitocin tattaunawa kan tsaro, harkokin soja, makamashi da sadarwa. A jawabin buɗe taro, Daraktan MIT Academy, Farfesa Talha Köse, ya ce taron zai mayar da hankali kan ƙalubalen Afirka a yau, yana jaddada cewa abin da ke faruwa a nahiyar na shafar duniya baki ɗaya. Ya ƙara da cewa Turkiyya ba ta kallon Afirka a matsayin filin gogayya ko ribar gajeren lokaci, illa tana ɗaukar ƙasashen Afirka a matsayin abokan hulɗa masu matsayi ɗaya, bisa ƙa’idar “Maganin Afirka ga matsalolin Afirka.”
A nasa jawabin, Ministan Shari’a na Somalia, Moallim Mahmoud Sheikhali, ya ce tattaunawar ta zo a lokacin da alaƙar Turkiyya da Afirka ta kai matakin dabaru da ke buƙatar zurfi da hulɗa mai tsari. Ya bayyana alaƙar a matsayin wadda ta bambanta da ta tsoffin ƙasashen mulkin mallaka, domin an gina ta bisa girmama juna, amfanin juna da haɗin gwiwa—ba tilastawa ko cin zarafi ba.
Sheikhali ya ƙara da cewa Turkiyya ta taka muhimmiyar rawa a Yankin Hancin Afirka, musamman ta goyon bayan Somalia wajen yaƙar ta’addanci, ƙarfafa tsaron teku da magance laifukan da suka ketare iyaka. A cewarsa, Afirka na buƙatar zaman lafiya da sahihan haɗin kai, kuma Turkiyya ta dade tana kasancewa abokin ci gaba da bangarorin biyu ke cin moriya.
Majiyar Labari: TRT HAUSA














