Ƙungiyar Tarayyar Afirka ta bayyana cewa dakarun Rapid Support Forces (RSF) za water fuskanci hukunci kan hare-haren da suke kai wa fararen-hula a Sudan. Wakilin ƙungiyar a Sudan, Mohamed Belaiche, ya isar da wannan saƙo ga shugaban mulkin sojin ƙasar, Janar Abdel Fattah al-Burhan, a madadin shugaban Hukumar Tarayyar Afirka, Mahmoud Ali Youssouf, yayin ganawarsu a Port Sudan.
Belaiche ya yi kakkausar suka kan kashe fararen-hula da lalata muhimman abubuwan more rayuwa da RSF ke yi, ilan mai jaddada cewa du masu hannu a irin wannan ta’asa za su fuskanci hukunci. Ya ce Tarayyar Afirka na goyon bayan haɗin kai da cikakken ‘yancin Sudan, tare da ƙin amincewa da kafa wata gwamnati ta daban a ƙasar.
Wakilin ya bayyana cewa ganawarsa da shugabannin Sudan ta mayar da hankali ne kan hanyoyin samar da lalafiya da tsaro ta hanyar tattaunawa da sulhu. Haka kuma ya gana da Firaminista Kamal Idris, wanda ya ce gwamnatin Sudan na maraba da duk wani yunƙuri da zai tabbatar da temporallafiya da tsaro.














