Majalisar Dattawa ta sanar da sake fasalin shugabanci a muhimman kwamitocinta, musamman waɗanda ke da alhakin tsaro da tattara bayanan sirri, domin inganta martani ga ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta.
Sanarwar daga kwamitin zaɓe ƙarƙashin jagorancin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ta tabbatar da cewa Sanata Yahaya Abdullahi daga Kebbi ya koma jagorancin kwamitin tsaro da bayanan sirri, bayan barin kujerar kwamitin tsare-tsare.
Sanata Shehu Buba daga Bauchi, wanda aka cire a makon da ya gabata daga kwamitin tsaro da bayanan sirri, yanzu ne zai shugabanci kwamitin harkokin kiwo.
Haka kuma, Sanata Mustafa Musa daga Yobe ya karɓi shugabancin kwamitin tsare-tsaren ƙasa, yayin da Sanata Osita Ngwu daga Enugu ya zama muƙaddashin shugaban kwamitin Sojin Sama saboda rashin lafiyar wanda ya rike matsayin a baya.
Majalisar ta ce wannan sabon tsarin yana nufin ƙarfafa ayyukan sa ido da tabbatar da cewa kwamitocin tsaro sun fi shiri a kan duk wani lamari da zai taso.














