Gwamnatin Ghana ta sanar da soke dokar da ta bai wa kamfanoni damar haƙar ma’adinai a cikin dazukan da aka killace, a wani mataki na dakile haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba da ake kira galamsey. An fara aiwatar da soke dokar ne daga ranar 10 ga Disambar 2025, lamarin da masu fafutukar kare muhalli da ƙungiyoyin farar-hula suka bayyana a matsayin gagarumar nasara bayan dogon lokaci na adawa da dokar.
Dokar L.I. 2462 ce ta ba da wannan dama, abin da ya haifar da fargaba game da lalacewar muhalli da rushewar gandun daji. Janye dokar na da burin dawo da kariya ga gandun daji, tare da ƙarfafa matakan yaƙi da haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba a faɗin ƙasar.
Ministan Filaye da Albarkatun Ƙasa, Emmanuel Armah-Kofi Buah, ne ya gabatar da matakin soke dokar a gaban Majalisa, inda ya jaddada muhimmancin kare gandun dajin Ghana. Ƙungiyar A Rocha Ghana da kuma wasu ƙungiyoyin farar-hula 17 sun yi maraba da matakin, suna yabawa ministan da gwamnati tare da kira da a ɗauki ƙarin matakai domin farfaɗo da gandun dajin da hakar ma’adinai ta lalata.














