Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa ta shawo kan saɓanin diflomasiyya da ya taso tsakaninta da Amurka dangane da matsalar rashin tsaro, bayan kalaman Shugaba Donald Trump na zargin azabtar da Kiristoci da kuma yin barazanar ɗaukar matakin soja. Wannan saɓani ya taso ne bayan Trump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Nijeriya na fuskantar abin da ya kira “kisan ƙare dangi” sakamakon tabarbarewar tsaro.
Ministan Yaɗa Labarai na Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce an warware lamarin ne ta hanyar tattaunawa mai girmamawa da fahimtar juna, wanda ya ƙara ƙarfafa alaƙar diflomasiyya tsakanin ƙasashen biyu. Ya jaddada hakan ne a wani taron manema labarai na ƙarshen shekara da aka gudanar a Abuja.
Gwamnatin Nijeriya tare da masana masu zaman kansu sun yi watsi da fassarar matsalar tsaron ƙasar a matsayin rikicin addini, suna mai cewa matsalar ta shafi ‘yan ta’adda da ‘yan fashi da makami musamman a arewacin ƙasar.
Bayan wannan, Nijeriya ta karɓi tawagar ‘yan majalisar dokokin Amurka a farkon watan, duk da cewa kwanan nan Amurka ta sanya Nijeriya cikin jerin ƙasashen da aka ɗora wa takunkumin biza. Idris ya kuma kare wata sabuwar yarjejeniyar agaji da Amurka za ta bayar ta dala biliyan 2.1, yana mai cewa amfanin tallafin zai shafi dukkan ‘yan Nijeriya ba tare da nuna bambanci ba.














