‘Yan Nijeriya da dama sun wayi gari da labarin da ya tayar da hankula, bayan da gwamnatin Amurka ta sanar da dakatar da bayar da biza ga ‘yan ƙasar daga ranar 1 ga Janairun 2026. Sanarwar, wadda Ofishin Jakadancin Amurka a Nijeriya ya fitar, ta nuna cewa matakin zai shafi nau’ikan biza da dama, lamarin da ka iya shafar ɗalibai, matafiya da masu neman dama a ƙasar Amurka.
Sanarwar ta bayyana cewa an dakatar da nau’ikan biza da suka haɗa da B-1/B-2 (na kasuwanci da yawon shakatawa), F, M, J (na ɗalibai da musayar maziyarta), da kuma bizar ‘yan gudun hijira. Nijeriya na cikin ƙasashe 19 da wannan mataki ya shafa, ciki har da Angola, Cuba, Venezuela, Senegal da wasu ƙasashe.
Sai dai gwamnatin Amurka ta ware wasu rukuni daga wannan mataki, ciki har da masu fasfon wata ƙasa daban, mazauna na dindindin bisa ƙa’ida, mahalarta wasanni na kasa da kasa, da kuma wasu rukunin ‘yan tsiraru daga Iran.














