A yau Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (CAF) ta tabbatar da cewa kocin Nijeriya, Eric Chelle, shi ne gwarzon koci a zagayen rukuni na gasar AFCON 2025, bayan bajintar da ya nuna wajen jagorantar Super Eagles cikin nasarori a dukkan wasanninsu na rukuni.
CAF ta bayyana wannan ne a cikin sanarwar da ta fitar game da jerin gwarazan ‘yan wasa goma sha ɗaya tare da kocin da suka fi fice a zagayen rukuni bayan buga jimillar wasanni 36. A cikin jerin ‘yan wasan da suka haskaka har da Mohamed El Shenawy na Masar, Riyad Mahrez na Aljeriya, Sadio Mané na Senegal, da Amad Diallo na Ivory Coast.
Daga tawagar Najeriya kuwa, Ademola Lookman ya samu matsayi a matsayin ɗan wasan tsakiya mai kai hari daga gefen hagu, inda ya zura ƙwallaye biyu a cikin wasanni uku da ya buga.
Najeriya ta kammala zagayen rukuni da maki 9 bayan doke Tanzania 2-1, Tunisia 3-2, da Uganda 3-1. Ita ce ɗaya daga cikin ƙasashe biyu kawai tare da Aljeriya da suka gama da cikakkun maki.
Eric Chelle ya jagoranci tawagar cikin ƙwarewa, inda Super Eagles suka ci ƙwallaye guda takwas, mafi yawa a zagayen rukuni. Wannan shi ne karo na farko da yake jan ragamar tawagar a babbar gasa tun bayan nada shi a Janairu 2025. Zagayen rukuni na AFCON 2025 da ake bugawa a Maroko ya kammala cikin birgewa.














