Nijeriya Tsaro

Fiye da Mutane 50 Sun Rasa Rayukansu a Harin ’Yan Bindiga a Jihar Neja

Harin ’yan bindiga a kauyen Demo na Jihar Neja ya yi sanadin mutuwar fiye da mutane 50, lamarin da ya jawo umarnin gaggawa daga Shugaba Tinubu kan tsaro da ceto.

Newstimehub

Newstimehub

5 Jan, 2026

6c73db6ca95809e75393ee381777a50dc5d3055a4d37968fcda42e89ebba787e

Harin ’yan bindiga ya sake girgiza al’ummar Jihar Neja, inda daruruwan mazauna yankin suka wayi gari cikin jimami sakamakon kisan gillar da aka yi a wani ƙauye na jihar.

Fiye da mutane 50 ne suka mutu bayan wasu ’yan bindiga dauke da makamai sun kai hari Kasuwar Daji da ke kauyen Demo a Jihar Neja, a tsakiyar Nijeriya. A cewar mazauna yankin, harin ya faru ne ranar Asabar, inda maharan suka buɗe wuta ba tare da bambanci ba, suka kashe mutane da dama tare da yin garkuwa da wasu.

Baya ga kisan, ’yan bindigar sun kuma sace kayan abinci da dukiyoyi daga kasuwar, yayin da aka garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibitoci daban-daban. An gudanar da jana’izar jama’a ga yawancin waɗanda suka rasa rayukansu a harin.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah-wadai da harin, yana mai bayyana cewa maharan sun ƙalubalanci juriyar ƙasa. Ya umarci jami’an tsaro da su gano tare da cafke duk waɗanda suka aikata laifin, tare da tabbatar da cewa za su fuskanci hukunci bisa doka.

Tinubu ya kuma ba da umarni ga hukumomin tsaro da su yi gaggawar ceto duk mutanen da aka sace yayin harin. Jihar Neja dai na fama da hare-haren ta’addanci a lokuta da dama, musamman a yankunan karkara da ke kusa da dazuzzuka da ’yan bindiga ke amfani da su a matsayin mafaka.

A baya-bayan nan, a ranar 21 ga Nuwamba bara, ’yan bindiga sun sace mutane 315, ciki har da dalibai 303 da malamai 12, daga makarantar Katolika ta St. Mary da ke Papiri a Karamar Hukumar Agwara. Duk da cewa wasu dalibai sun tsere a ranar harin, daga baya gwamnatin tarayya ta tabbatar da sakin sauran waɗanda aka sace zuwa ƙarshen watan Disamba.

Majiyar Labari; TRT HAUSA