Nijeriya Tsaro

Hatsarin Kwale-kwale a Yobe: Sojojin Nijeriya Sun Ciro Gawarwaki 27

Hatsarin kwale-kwale a Nguru, jihar Yobe, ya yi sanadin mutuwar mutane 27 yayin da sojojin Nijeriya suka ceto 13 da ransu.

Newstimehub

Newstimehub

5 Jan, 2026

94ea9fe2fe2c592dedeec139579613e1e87c3205a381e37748f72af18716a323

Hatsarin kwale-kwalen da ya faru a Nguru ya sake jaddada barazanar tafiye-tafiye ta ruwa a yankin, inda sojoji da hukumomin ceto suka yi gaggawar ceto rayuka tare da ciro gawarwaki, yayin da ake kira ga ƙarin matakan tsaro.

Wata majiya daga rundunar sojin ƙasa ta shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12:15 na dare a ranar Lahadi, 4 ga Janairun 2026, lokacin da kwale-kwale mai ɗauke da ‘yan kasuwa kimanin 40 daga ƙauyen Adiani a jihar Jigawa ke kan hanyarsa zuwa wata kasuwa a Nguru.

Majiyar ta ce kwale-kwalen ya kife ne a yankin kogin Garbi, lamarin da ya jawo salwantar rayuka da dama. Bayan samun rahoton aukuwar hatsarin, dakarun Bataliya ta 241 tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro da masu nutso na cikin gida suka gaggauta zuwa wurin domin aikin ceto.

“Aikin haɗin gwiwar bincike da ceto ya yi nasarar ceto mutum 13 da rai, yayin da aka ciro gawarwaki 27 daga cikin kogin,” in ji majiyar.

An riga an binne waɗanda suka rasa rayukansu bisa koyarwar addinin Musulunci, yayin da hukumomin da abin ya shafa ke ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace don kauce wa sake aukuwar irin wannan hatsari.

Majiyar Labari: TRT HAUSA