Matar Firayim Ministan Malaysia, Wan Azizah Ismail, ta kai ziyara a Gidan Al’adu na Afirka da Kasuwar Dabaru da ke birnin Ankara, inda ta duba kayayyakin sana’o’in mata daga ƙasashen Afirka 41 da aka tanadar a wurin. Ta je tare da Ministan Harkokin Iyali da Jin Kai ta Türkiye, Mahinur Ozdemir Goktas, da shugabar kwamitin gudanarwa na Gidan Al’adu na Afirka, Zeliha Saglam. Ziyarar ta kasance a gefen ziyarar aiki da Firayim Ministan Malaysia, Anwar Ibrahim, ke yi a Türkiye.
A lokacin ziyarar, an gabatar da bayanai kan tarihin kafuwar cibiyar tun 2016 da kuma muhimmiyar rawar da take takawa wajen ƙarfafa musayar al’adu, tallafawa sana’ar hannun mata da kuma samar da dandalin haɗin kai ga diplomasiyyoyi da daliban Afirka da ke Türkiye. Wan Azizah ta yaba da ingancin kayayyakin da ta gani, tare da jinjinawa irin gudummawar da uwar gidan Shugaban Türkiye, Emine Erdogan, ke bayarwa wajen karfafa alakar ƙasashen Afirka da Türkiye.














