Shugaban kasar Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya taya ‘yan jarida murnar Ranar ‘Yan Jarida masu aiki ta 10 ga Janairu, yayin wata ziyara da ya kai unguwar Beyoglu da ke birnin Istanbul a ranar Asabar.
Erdogan ya gana da manema labarai a wurin ziyarar, inda ya yaba da rawar da suke takawa wajen isar da sahihan labarai ga al’umma tare da yi musu fatan alheri.
“A wannan rana ta musamman, muna farin cikin kasancewa tare da ku. Ina fatan za mu ci gaba da yin irin wannan taro na tsawon shekaru masu zuwa,” in ji shugaban kasar, yana yi wa ‘yan jaridar fatan samun nasara da albarka a aikinsu.
A yayin ziyarar, Erdogan ya samu rakiyar Ministar Iyali da Ayyukan Jama’a Mahinur Ozdemir Goktas, Ministan Al’adu da Yawon Bude Ido Mehmet Nuri Ersoy, da Daraktan Sadarwa na Fadar Shugaban Kasa Burhanettin Duran.














