A yayin da yanayin tsaro ke ƙara ɗaukar zafi a Gabas ta Tsakiya, Iran ta aika da saƙo mai ƙarfi ga dukkan ƙasashen da ke maƙwabtaka da ita, tana mai cewa ba za ta lamunci a yi amfani da ƙasarsu ko sararin samaniyarsu wajen kai mata hari ba, bayan isowar ayarin jiragen yaƙin Amurka zuwa yankin.
Mataimakin kwamandan rundunar sojin ruwa ta IRGC, Mohammad Akbarzadeh, ya ce duk wata ƙasa da ta bari a yi amfani da filayenta, tekunanta ko sararin samaniyarta wajen kai hari kan Iran za a ayyana ta a matsayin “abokiyar gaba”. Wannan gargaɗi ya zo ne bayan shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa ana tura ayarin jiragen yaƙi masu ɗauke da jiragen sama kusa da Iran, yana kuma fatan cim ma yarjejeniyar diflomasiyya da Tehran.
Kalaman Trump sun ƙara tayar da hankula a yankin, inda Iran ke ganin wannan motsi a matsayin barazana kai tsaye ga tsaron ƙasarta.














