Nijeriya da Jamhuriyar Türkiye sun sabunta alkawarin ƙarfafa hulɗa da ’yan ƙasashensu da ke ƙetare ta hanyar sanya hannu kan Yarjejeniyar Fahimta (MoU) da ta shafi harkokin diaspora. An rattaba hannu kan yarjejeniyar ne a yayin ziyarar aiki ta Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu zuwa Türkiye.
A madadin Nijeriya, Ministan Ƙasa na Harkokin Waje, Bianca Odumegwu-Ojukwu, ce ta sanya hannu, yayin da Ma’aikatar Harkokin Wajen Türkiye ta wakilci gwamnatin Ankara. Ta ce MoU ɗin ya samar da tsari na musayar ilimi, kwarewa da kyawawan dabaru wajen tafiyar da harkokin diaspora, tare da ƙarfafa ziyarce-ziyarce, shirye-shiryen haɗin gwiwa da taruka.

Yarjejeniyar ta tanadi fannoni na haɗin kai da suka haɗa da shigar diaspora cikin tsara manufofi, haɓaka zuba jari, wasanni, al’adu da ilimi, da kuma haɗin gwiwa a kimiyya da fasaha. Haka kuma, ta mayar da hankali kan kare jin daɗin ’yan ƙasa a ƙetare, tallafa wa musayar al’adu da ilimi, da ƙarfafa haɗin gwiwar tattalin arziki.
Shugaban hukumar Ministry of Turks Abroad, Abdulhadi Turus, ya yabawa yarjejeniyar yana mai cewa za ta ƙarfafa alaƙa tsakanin al’ummomin diaspora na Nijeriya da Türkiye a duniya. Ya kuma tuna cewa ɗaruruwan ɗaliban Nijeriya sun amfana da shirin Türkiye Scholarships tun 1992, inda dubban ke karatu a ƙasar a yanzu.














