Ƙasar Somalia ta samu kujera a Kwamitin Zaman Lafiya da Tsaro na African Union (PSC) karo na farko tun bayan kafa kwamitin a 2004. Za ta yi wa’adi daga 2026 zuwa 2028 bayan zaɓen da aka gudanar a Addis Ababa, gabanin taron koli na AU. Kwamitin PSC na da alhakin hana rikice-rikice, daidaita su da kuma nemo mafita ga matsalolin tsaro a nahiyar.
Zaɓen na zuwa ne bayan Somalia ta ƙaddamar da takararta a 2025 tare da kamfen diflomasiyya na neman goyon bayan ƙasashe mambobi. Jami’ai sun bayyana nasarar a matsayin alamar dawowar ƙasar cikin harkokin diflomasiyyar Afirka bayan shekaru na rikici da rashin daidaito.
AU dai ta shafe fiye da shekaru 17 tana gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya a Somalia, tana tallafa wa gwamnati wajen yaƙi da ta’addanci da ƙoƙarin daidaita ƙasa.
Majiyar Labari: TRT AFRIKA














