Afirka

Libya ta ayyana zaman makoki na kwana uku bayan rasuwar Babban Hafsan Sojojin ƙasa

Libya ta sanar da zaman makoki na ƙasa na kwanaki uku sakamakon hatsarin jirgin sama a Turkiyya da ya yi sanadiyyar mutuwar Babban Hafsan Sojojin ƙasar da wasu manyan jami’an soji.

Newstimehub

Newstimehub

24 Dec, 2025

64905d507d656bed6a4bf2486240e7bf36315ba24cf0903053a9eab520fa670a e1766598541516

Cikin alhini da jimami, Libya ta ayyana zaman makoki na ƙasa bayan wani hatsarin jirgin sama a Turkiyya da ya yi sanadiyyar rasuwar Babban Hafsan Sojojin ƙasar, Mohammed al-Haddad, tare da wasu manyan jami’an soji.

Gwamnatin Haɗin Kan Ƙasa ta Libya ta sanar a ranar Talata cewa za a yi zaman makoki na kwanaki uku, inda za a sauke tutoci rabin sanda a dukkan cibiyoyin gwamnati, tare da dakatar da duk wasu taruka da bukukuwa na gwamnati.

A cikin sanarwar, gwamnati ta miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan da abokan aikinsu a Rundunar Sojin Libya, tana mai addu’ar Allah ya ji ƙansu kuma ya ba iyalansu haƙuri.

Shugaban Majalisar Shugabancin Libya, Mohamed Menfi, ya bayyana mutuwar a matsayin “babban rashi ga rundunar soji da al’ummar ƙasa,” yana mai yabawa mamatan bisa sadaukarwa, jajircewa da biyayya wajen hidimar ƙasa.

A nasa ɓangaren, Ministan Cikin Gida na Turkiyya, Ali Yerlikaya, ya ce an gano ɓaraguzan jirgin haya samfurin Falcon 50 a kudancin Haymana, kusa da Ankara, inda jami’an Turkiyya suka tabbatar da mutuwar Babban Hafsan Sojojin Libya da wasu jami’ai hudu.

Majiyar labari: Trt Hausa