Kafafen yaɗa labarai a Ethiopia sun mayar da hankali kan ziyarar da shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan zai kai Addis Ababa, ziyarar da ake kallon mai muhimmanci a fannin diflomasiyya. Ziyarar na zuwa ne yayin da kasashen biyu ke murnar cika shekaru 100 da buɗe ofishin jakadancin Turkiyya a Ethiopia, alaka mai dogon tarihi tun ƙarni na 16.
Kafafen gwamnati da masu zaman kansu sun bayyana ziyarar a matsayin wata dama ta ƙarfafa dangantakar siyasa da tattalin arziki. Rahotanni sun nuna cewa ana sa ran sanya hannu kan sabbin yarjejeniyoyin haɗin gwiwa, musamman a fannoni kamar kasuwanci, ababen more rayuwa da tsaro.
Masana sun jaddada cewa dangantakar Turkiyya da Ethiopia ta ginu ne kan fahimtar juna da tattaunawa kai-tsaye. Wasu masu sharhi sun ce rawar da Ankara ke takawa a rikice-rikicen yankin Kusurwar Afirka na daga cikin dalilan da suka sa alakar ke kara ƙarfi.
Haka kuma, an yi nuni da muhimmancin diflomasiyyar al’adu, inda shirye-shiryen talabijin na Turkiyya da daliban Ethiopia da suka yi karatu a Turkiyya ke taimakawa wajen inganta fahimtar juna tsakanin al’ummomin kasashen biyu.
Majiyar Labari: TRT AFRIKA














