Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya bayyana cewa yadda aka gudanar da zaben Federal Capital Territorycikin lumana ya nuna jajircewar mazauna yankin ga dimokuradiyya. A wani jawabi na musamman, ya ce sakamakon zaben ya nuna cewa jama’a sun fi fahimtar siyasar kasar nan fiye da da.
Wike ya soki wasu ‘yan siyasa da ke amfani da dabarun kamfen kamar sayen masara da gyada a bakin hanya, yana mai cewa irin wadannan abubuwa ba su da tasiri wajen yaudarar ‘yan Najeriya. Ya jaddada cewa mazauna FCT sun nuna ba za a iya ruɗarsu da abin da ya kira “emergency democrats” ba.
Ministan ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai cewa zaben ya nuna hangen nesan jagorancin sa da tasirin manufofin Renewed Hope Agenda. Haka kuma ya taya Independent National Electoral Commission murna kan gudanar da zabe mai inganci, tare da yabawa hukumomin tsaro kan tabbatar da zaman lafiya.
Ya bukaci wadanda suka yi nasara su yi aiki da kaskantar da kai tare da mayar da hankali kan ci gaban al’umma, yayin da ya gode wa mazauna FCT, musamman na garuruwan da ke kewaye, bisa fitowa da suka yi cikin tsari da lumana.














