Gwamnatoci da ƙungiyoyi a duniya sun nuna damuwa yayin da rikicin da ya ƙara tsananta tsakanin Amurka, Isra’ila da Iran ke ci gaba, inda Nijeriya, Senegal da Libya suka yi kira da a dakatar da tashin hankali.
Sun jaddada bukatar a koma ga tattaunawa da bin dokokin ƙasa da ƙasa don kauce wa ƙarin rarrabuwar hankali da tabarbarewar zaman lafiya a yankin.
Nijeriya ta bayyana cewa hauhawar hare-haren na iya haifar da mummunar illa ga yankin da duniya baki ɗaya, yayin da Senegal ta yi Allah wadai da amfani da ƙarfi kuma ta jaddada cewa diflomasiyya ita ce hanya mafi inganci don cimma zaman lafiya.
Libya kuma ta ce hare-haren da ake kai wa ba za a iya yarda da su ba, tare da kira ga sasanta rikici ta hanyar tattaunawa maimakon amfani da makamai.
A gefe guda, wasu ƙasashe sun fara ɗaukar matakan kariya. Ghana ta fara kwashe ma’aikatan ofishin jakadancinta daga Tehran tare da gargadin ‘yan ƙasarta a wasu ƙasashen yankin da su takaita zirga-zirga.
Haka kuma, Ƙungiyar Tarayyar Afirka da ECOWAS sun yi kira da a dakatar da tashin hankali, suna nuna cewa yaƙi zai iya dagula kasuwannin makamashi, cinikayya da samar da abinci a duniya.
Rikicin ya ɓarke ne da sassafe bayan Isra’ila da Amurka sun kai hare-hare kan birane da dama a Iran, wanda Isra’ila ta kira “harin rigakafi.” Daga nan ne Iran ta mayar da martani da harba makamai masu linzami zuwa Isra’ila tare da kai hari kan wasu sansanonin Amurka a yankin. An rufe sararin samaniya a ɓangarorin biyu, yayin da fararen hula ke fuskantar fargabar abin da zai biyo baya.














