Kimanin mutane 100,000 sun bar Tehran cikin kwanaki biyu bayan fara rikici tsakanin Iran da abokan gabarta, a cewar rahoton UNHCR. Hukumar ta ce hare-haren da aka kai a ƙarshen watan Fabrairu ne suka haifar da tsoro da rashin tabbas a babban birnin kasar.
Duk da hijirar da mutane ke yi a cikin ƙasar, jami’an Majalisar Dinkin Duniya sun ce har yanzu ba a samu karuwar mutanen da ke tsallaka iyakokin ƙasashe ba. Haka kuma an ce komai yana tafiya yadda ya kamata a mashigar iyaka ta Islam Qala Border Crossing tsakanin Iran da Afghanistan.
Rikicin ya fara ne bayan hare-haren soji da aka kai kan wurare a Iran wanda ya jawo ramuwar gayya da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙi a sassan Gabas ta Tsakiya. Masana na gargadin cewa rikicin na iya ƙara faɗaɗa zuwa wani babban rikicin yankin yayin da hare-hare ke ci gaba.














